Total Pageviews

Tuesday, June 7, 2011

Sharhi Na 7. Talaucin Arewa, Dalilansa da Maganinsa

SHARHI NA 7
LALACEWAR AREWA (2)

TALAUCI, DALILINSA DA MAGANINSA

Dan Arewa yau ya zama abun tsana, wariya da tsangwama a Najeriya ba don komai ba sai don ya fi kowa talauci. In ka musa, lura da abu daya. Ka taba ganin mai kudin da ba a haba haba da shi? Da zarar ka yi kudi, a ko’ina a duniya, mutane ba za su damu da asalinka ko halinka ba. Nan da nan zaka zama abokin shawarar sarki, malamai za su rika jawo nassi suna gaskata maganarka ko karya ce ka shara. Sai kaji sun ce, “Aiko mun gani a hadisi,” in Dan Ibro a wakarsa ta Bayanin Naira. Jama’an gari kuwa kowa na matsowa kusa da kai don ya samu abun lasa. In ka nemi ‘ya za a baka. In ka bada shawara za a dauka. In ka yi fada za a ji. Kudi ke nan. Mai Maqamatul Hariri kam da ya gama yiwa kudi kirari, sai ya rufe da cewa “ba don tsoron Allah ba, da na ce kudi sun fi komai iko.”

To in ‘yan Arewa na son dawo da martabarsu, bayan baiwa ilmi muhimmanci da aiki da shi, abu mafi na biyu shi ne su bi ilmin nan ya nuna musu hanyar samun arzikin duniya. Da razar arzikinsu ya bunkasa, to sauran hakkokinsu na siyasa da zamantakewa za su biyo baya cikin ruwan sanyi. In ko suka ci gaba da gudun duniya, to wallahi, ba hakkin da za su samu sai bauta a Najeriya da duniya baki daya. Da talaucin za a yi amfani a hana musu komai kamar yadda muka gani a zaben da ya gabata. Mutane suka rika karbar naira hamsin ko indomi suna jefa kuri’arsu inda ba nan suka so ba.

Amma kafin a san hanyar korar talauci ya kamata a san ta ina ya lallabo ya shige mu don mu toshe wannan hanya komai wuyarta. Akwai dalilai da yawan gaske wanda masu ilmin tattalin arziki suka zana. Na sha tattaunasu a rubutu na na turanci. Amma zan ambace su a takaice a nan. Nan gaba zan zabi wasu daga cikinsu in yi cikakken bayani akan kowannensu.

1. Rashin Gaskiya.

Ba abun da ya jawo mana talauci irin rashin gaskiya. Dukiya ba ta habaka sai an rike ta da gaskiya kamar yadda za a yi kokarin rike kwai a kwando. In aka sa rashin gaskiya, walau ta hanyar sace ta, ko hadata da haramiya irin su algus, da tauye awo, da cin hanci, da sauransu, to dole dukiyar ta tawaya. Wadannan abubuwan kuwa sun zame mana ruwan dare a nan Arewa. Masu sai da nama, masu awo, masu sai da mai, kowa aikinsa ke nan, ya sai da jabu, ko ya rage awo.

In da gaskiya da himma, Allah shi zai sa albarka a kasuwancin. Duk maikudi na son kudinsa su habaka. In da da gaskiya, da masu kudi sun rika baiwa ‘yan Arewa jari. Su kuma su sarrafa shi akan gaskiya da amana, da ilmi da himma. Zasu yi kokarin habaka dukiyar don su ma su amfana. Kafin shekara, naira miliyan daya sai ya dawo miliyan biyu ko fiye. Da haka dukiyar Arewa za ta yi ta habaka. Kafin a ce karni guda, wannan sashe na Najeriya ya mallaki tattalin arzikinsa. Rayuwa ta inganta, talauci ya tattara komatsansa ya bar gari.


Mu duba daga Inyamurai da Yarbawa. In sun aje yaro a shago da wuya zai saci dukiyarsu. Daga nan shagunansu suke karuwa har shima yaron a sallame shi ya bude nasa kasuwancin. An ci Inyamurai da yaki, aka bar masu arzikinsu da naira ashirin kacal, amma yau ta hanyar himma da gaskiya tsakaninsu, sun fi kowa a Najeriya dukiyar kasuwanci. Ga yahudawa nan. Basa cutar junansu. Ta hanyar hada kai da gaskiya tsakaninsu, yau ba wanda ya fi su arziki da fada aji a duniya. Da mu inyamurai suke misali da mu wajen rike amana. Amma yau sai tofin Allah tsine. Ko shiga motar hayarmu ba su son yi.

In munki gaskiya, ko anyi shekara dubu ana karbo kudi daga Abuja, ko ‘yan kasuwanmu na zuba jari, ba abun da zai karemu da shi sai tsiya, kamar an shuka dusa. Abu na farko ke nan.

2. Lalaci

Malam bahaushe ya yi kaurin suna wajen lalaci na tunani da aiki. A karshe sai ya jinginawa Allah sakamakon lalacinsa ya ce, “Allah ne ya sa haka. Kaddara! Duniya dama ba wajen jin dadin mumini ba ne.” Gudun duniya a gunsa shi ne tsoron Allah. Yana da saurin aminta da kalilan. Don haka in ya samu kadan sai ya rage himma.

Irin wannan tunani da ya shigi musulmi a duniya duka dole a koreshi. Allah ya kawo mu duniya ne don mu rayu a cikinta. Rayuwa kuwa tushenta tattalin arziki ne, don inda baki ya karkata, nan yawu yake zuba. In bamu tashi muka baiwa duniya hakkinta ba, to muna da bauta a gabanmu. Dole burin kowannenmu ya zame kyautata halin rayuwarsa ta duniya ta hanyar da zai tsira da mutuncinsa da na addininsa, wanda haka ba zai samu ba sai ya fita daga kangin talauci.

Bayan haka, dole mu lura cewa muna zaune a duniya tare da sauran al’ummomi. In su suna da himma, mu bamu da ita, to arzikin kasa zai koma wajen masu himma ne. Mu kuwa a barmu da allazi wahidun, kamar yadda muke yi yau.

A yau abunda yake faruwa kenan a Najeriya. Gamu nan da yara facaca marasa aikin yi don kawai ba su so su sha wuya. Iyayensu sun kawo su duniya suna ta bauta musu. Sun ki sa su harkar noma, ko kira, ko dukanci da sauran sana’o’i. Ga ruwan sama Allah na saukarwa duk shekara, ga filaye bila adadin, amma sun taru a birni ba su da niyyar kaura zuwa inda za su amfani kansu, sai dai iyayensu su ciyar da su. Masu zuwa gonar ma in hantsi ya yi sai su dawo gida. Balle a ce kaka ta shigo. Kadan ne suke noman rani. An barwa ‘yan lambu. Sauran jama’ar gari kuwa sai zaman banza duk tsawon rani, alhali ga koguna da dam dam masu yawa da Allah ya albarkaci Arewa da su.

Hakanan manyan ma. Kowa ya tare a kwangila da cin kudin jama’a a cikin gwamnati. An ki a bi hanya mai wuya irin noma da kiwo tunda ga kudin banza nan na fetur. Kalilan ne suke kafa masana’antu su tsaya da kansu, su hakura da kadan din da ake samu, don sauran mutane su amfana da aikin yi, ko har abun ya bunkasa.

A karshe karatun boko ya zo ya kara lalata zuciyar yaranmu. A wurinsu, aikin ofis shi ne aiki, ko a kamfani ko a gwamnati. Shi suke jira. Shi ma sai mai maiko. In ya zo, su yi. In bai zo ba, suna nan zaune suna kirga kansu cikin marasa aikin yi, iyayensu na ci da su, suna musu aure da sauran shagwaba.

Ina ga lokaci ya yi da za a nunawa mutane ba hakkin gwamnati ba ne samar wa kowa aikin yi. Aikinta ta wanzar da yanayin neman arziki. Daga nan kowa sai ya tashi tsaye, tashi ta fissheshi. Dalilin da ya sa ke nan in ‘yan siyasa sun yi alkawarin samarwa dukkan yara aikin yi suke gagara. Ba za su iya ba, don ba huruminsu ba ne.

Don haka iyaye su daina sagarta ‘ya’yansu. Yara kuwa su san cewa duniya ba ta rago ba ce. Duk wanda ya zota, dole ya tashi tsaye. Malamai kuwa su daina kashe zuciyar mutane da wani tauhidi da bashi da amfani komai asalinsa. Nan duniya muke. Ita muka sani. Ita ke da tasiri a rayuwarmu. Ta hanyarta za mu iya yin addinin cikin martaba da kamala. Wanda ke son lahira kawai, to ya jira ya mutu, ya daina kukan talauci. Gwamnati kuwa ta rika gayawa mutane gaskiya. In za ta taimaka, ta taimakawa wadanda suka tashi tsaye, ba zauna gari banza ba.

Arewa mu kori lalaci. In ba haka ba bauta yanzu muka farata a Najeriya.


3. Danniyar Gwamnatin

Akwai alamu masu yawa da ke nuna cewa gwamnatin tarayya, wacce ita ke da hakkin tsara tattalin arzikin kasa da manufofinsa, bata baiwa abubuwan da tattalin arzikin Arewa ya kafu a kansu muhimmanci ba. In ka duba kasafin kudin kowane shekara, za ka iske harkar noma ba a kulata ba ko kadan. Noman nan kuwa da shi akasarin gidaje a Arewa suka dogara kuma ta hanyarsa ake ciyar da Najeriya. Alal misali, akwai shekarar da Obasanjo ya warewa harkar noma naira biliyan goma rak, a lokacin da ya kashe sama da naira biliyan saba’in wajen gina dandalin wasanni na kasa a Abuja. Wannan zalunci ne da ‘yan Arewa yakamata su yaka, kwansu da kwarkwarsu. To amma anbarmu masu sharhi kawai da korafi a jarida.

In an ware isassun kudi don aikin noma, ta nan za a samu a yi wa manoma rangwamen kanyan aiki (subsidy) irin su tarakta, da iri, da taki, da sauransu. Manoma za su samu wadannan abubuwa cikin sauki ta yadda nomansu zai zo da riba mai yawa don su kuma yinsa badi. Rashin yin haka, da rashin tsari na adalci wajen rabon duk wani abu da gwamnati za ta bayar, shi ya sa manyan manoma da kamfanoni suka yi watsi da noman, ganin asarar da suke tafkawa duk shekara. A karshe, an bar noman hannun masu karamin karfi wadanda bai wuce su noma bukatunsu na gida ba kawai.

Bayan rashin isasshen rangwame, gwamnatin tarayya ta zalunci Arewa sossai wajen sa dokokin da ke dakushe noman kansa. Ga mari ga tsinka jaka! Alal misali, ba abunda ya fi kasuwa habaka noma. In manomi zai sai da kayan gonarsa da daraja, shi ke nan, badi ma zai noma fiye da haka. To amma kasuwan hatsi, wanda shi ne akasarin abun da muke nomawa, sai gwamnati ta sa masa takunkumi, ta haramta fitar da shi kasashen waje. Don haka, masara da gero da shinkafa kullum sai an sai da su a farashin da bai kai abunda aka kashe wajen nomasu ba. In kaga an fitar da su sai ta hanyar sumogal. Kullum sai sun yi kwantai a Najeriya. Alhali kuwa kudu am basu dama su fitar da kayan masana’antunsu yadda suke so, su sayar a farashin da suke so. Wannan magudi ne. Da sakel!

A gaskiya wannan zalunci ne wanda aka assasa shi bisa tsohon karatu dake tsammanin in an bada dama a fitar da abinci, wai za a yi yunwa. Ba yunwar da za a yi tunda dai haka zai jawo noman ya bunkasa sossai. Wannan shi ne matakin da Afrika ta kudu ta dauka. Ban ga dalilin da za a maida ‘yan Arewa bayi ba suyi ta noma ba riba don kawai wadanda ba sa noma su wadata da abinci. Sannan kuma, sai a dawo ana zagin Arewar cewa ta cika talauci, da mabarata, da almajirai, da sauran bakaken maganganu.

To ba za ta sabu ba. Dole ‘yan Arewa su tashi su tabbatar da an canza wannan dokar. Da zarar an bamu dama mu fitar da abinci, to zamu noma da yawa yadda zai wadaci gida kuma mu sayarwa makwabta. Wannan zai kawo mana aikin yi mai yawa ya kuma habaka arzikinmu. Talakawa ba za su tawaya ba sai dai su kara arziki. Tunda manoma ne, za su noma abunda zai ishe su ci su sai da sauran a farashi mai tsoka. Su kuwa wadanda ba sa noma – mai’aikata, ‘yan kasuwa da ‘yan kudu, sai su tanadi kudin saye. Kan mage yaw aye. Ba zai yiwu abar fiye da kashi saba’in bisa dari na al’umma cikin bauta ba, saura kuwa suna holewa.

Abunda kawai za a yi sai a bada sanarwar shekarar da dokar zata fara aiki. Kowa sai ya shirya wannan daminar. Wanda ya yi lalaci, to yunwar da ta sameshi shi ya so.

Dokar hana fitar da hatsi a Najeriya dole a soke ta. In ba haka ba, za mu ci gaba da bautawa wasu ne kawai a Najeriya, muna sauwake musu rayuwa, su kuma suna mana kallon matalauta.

Yan majalisunmu na Arewa da duk mai son ci gaban tattalin arzikin ‘yan Najeriya, kalubalenku. Za mu nemi ku yi amfani da yawanku a majalisa wajen tabbatar da wannan burin.



Jama’a za mu dakata a nan. Za mu ci gaba da sharhi kan harkar noma da sauran abubuwan da gwamnati ke yi wajen haddasa talauci a Arewa. Allah ya taimaka.

7 June 2011

Monday, June 6, 2011

Sharhi na 6. Lalacewar Arewa (1) Watsi da Ilmi

SHARHI NA 6.
Na Dr. Aliyu U. Tilde

LALACEWAR AREWA (1):
WATSI DA ILMI

Ra’ayi tsakanin masu sharhi kan al’amuran yau da kullum ya daidaita kan cewa ganin yadda Arewa ta sha kaye a zaben da ya wuce, yakamata ‘yan Arewa suyi dogon nazari kan matsalolin da suka addabi wannan sashi na Najeriya da niyyar samun mafita a nan gaba. Ganin haka na yi niyyar jera sharhi kan al’amuran da nake ganin sune kan gaba wajen mai da Arewa baya. Kamar yadda aka saba, a ciki za mu tsage gaskiya ba tare da son rai ba ko tsoro. Sai mai karatu ya biyoni mu je zuwa…

Abu na farko da zan tattauna a kai shi ne yadda ‘yan Arewa suka yi watsi da ilmi. Wani zai ce “Ka ji dokata kuma. Ya zai ce mun yi watsi da ilmi bayan gashi jiddin wala hairan muna fadi tashi wajen ilmantar da yaranmu a makarantun addini da na boko, daga firamare har jami’ia? Yaya za a ce an yi watsi da ilmi idan a yau ana samun yawan masu digiri fiye da a kowane lokaci a cikin tarihinmu? Yaya za a ce ana watsi da ilmi bayan ga ma’aikatun ilmi suna gudanar da shi, ana daukar malamai aiki, masu wa’azi da kungiyoyin addini suna karuwa fiye da da?

Irin wadannan tambayoyi tabbas suna iya bijirowa a zukata kuma su makantar da mai nazari ga tunanin cewa in yara na zuwa makaranta, ana samun masu takardun shaida kala kala ko mahaddata kur’ani da malaman hadisi da malamai masu wa’azi shi ke nan al’umma tana baiwa ilmi hakkinsa. Abun ba haka yake ba.

Watsi da ilmi da muka yi shi ne mun mai da shi abun samun abinci. Ba ma nemansa don mu bunkasashi ta hanyar sabunta shi, da bincikensa da aiki da shi. Da zarar mun samu takardar shaidar fita daga makaranta, shi ke nan, mun jingine karatu. Ba sauran sayen littafi a fannin da muka karanta, ko bin diddigin sabon ilmin da ake wallafawa a ciki koda yaushe. Wanda muka karanta din ma ba ruwanmu da bitarsa, in dai ba abunda ya zama dole ba kamar ga malaman makarantu don koyarwa.

Haka kuma ba ruwanmu da fadada saninmu ta yadda za mu karanta wasu fannunnuka banda wandada muka kware a ciki koda kuwa wanda ke da dangantaka ne da su, wanda abu ne da ya zame wajibi ga dukkan wanda ke son sanin abunda duniya ke ciki ko ina ta nufa.

Hakanan kuma bamu damu da bincike kan ilmi ba don karuwarmu da duniya baki daya. Yan Arewa da suka yi fice don gano sabbin abubuwa na ilmi ko kirkiro fasaha wace duniya bata san da ita ba kalilan ne kwarai, in akwai ma.

A karshe, ba ruwanmu da aiki da ilmi. Hasali ma, mai ilmi gaba ake da shi a nan Arewa. Shi ba komai ba ne da za a waiwaya in matsala ta taso, ko za a saurari ra’ayinsa akan muhimman al’amura da za su yi tasiri bisa rayuwar jama’a. Abun da aka sa gaba bin son zuciya. Kudi sune komai. Sai a jingine ilmin a gefe, musamman a gwamnati, a karya doka, a take hakkin mutane, a tafka ta’asa wacce za ta hallaka al’umma don amfanin mutum daya ko biyu.

Ga misali, duk masu sata a gwamnati sun san komai game da illar satar da suke ga al’umma, walau ta kudi ko ta kayan morewar jama’a idan. Malami ya san satar alli, da takardu, da na’urorin bincike abu ne da zai gurgunta ilmi a makarantarsa, amma akasarin shugabannin makarantu sai su yi biris da ilminsu su yi ta dauke dauke a makarantun da aka basu amana. Haka jami’an asibiti da ke sace naurorin binciken likita da magunguna. Haka injiniyoyin da ke aiki a ma’aikatar ayyuka, wadanda ke aringizon kwangila ta yadda a maimakon kudin da ake da su su gina asibitoci shida, sai a bada su a ginin asibiti guda. Haka masu daukan ma’aikata, sai su dau maikatata bisa sanayya ko cin hanci su bar kwararru. In a makaranta ne sai a bar wanda yake da ilmi a dauki wani jaki wanda zai hallaka rayuwar yara akalla arba’in duk shekara tunda bai san abun da zai koya musu ba. In ka ce ayi amfani da sani, to ka zama abokin gaba.

Wannan hali namu na watsi da ilmi ta hanyoyi dabam dabam shi ya sa muke gagara fahimtar abubuwa idan suka taso mana, shi ya sa tattalin arzikinmu yake ja da baya ko yaushe, shi kuma ya sa al’ummomi da suke baiwa ilmi muhimmanci suke tsere mana a dukkn fannonin rayuwa.

Ashe ba abun mamaki ba ne muka zame al’umma wace ba ta son karatu. Ko mai karatu zai tuna yaushe ya je kantin litattafai don ya duba ya ga ko an kawo wani littafi da zai amfaneshi inba wanda yaransa za su yi amfani da shi a makaranta ba? Yaushe ne in ya je kasar waje zai dawo da akwati guda na sabbin litattafai da aka buga a cikin fanninsa?

Wannan sakaci shi ya sa aka samu karancin dakunan karatu da kantunan sai da litattafai da masu mawallafa a nan Arewa. A Arewa kaf, zai yi wuya ka samu kantin da, alal misali, ke sai da sabbin litattafai da aka wallafa a shekarar da ake ciki, koma a shekaru biyu da suka wuce. Duk litattafan ko dai na ‘yan makaranta ne ko tsoffi ne da aka yi gwanjonsu a kasashen waje don sun yi kwantai tun shekara goma ko talatin da suka wuce.

Akwai ranar da na nemi kundin tsarin mulkin Najeriya a Gombe da gaggawa don in yi amfani da shi wajen rubutu amma na rasa a kantunan garin kaf. Muhimmancin wannan kundi kuwa ya kai ace akwai shi fassare cikin hausa a kowane gida, bama a kanti ba. Hakaza kudayen dokoki dabam dabam. In an buga na zabe, ga misali, ya kamata a ce kowa na das hi, don mu san tanadin da zamu yi wajen cin zaben. Amma haka muke tinkarar abubuwa cikin jahilci. A karshe a mana zarra saboda lalaci wajen neman ilmi. Ina ga yayana Jega zai iya yin dogon sharhi akan wannan, tunda shi ganau ne ba jiyau ba.

Haka kuma ga dokar ‘yancin tambayar bayanan gwamnati an sa hannu a kanta satin da ya wuce. Yanzu haka za mu zauna tsawon shekaru ba wanda ya mallaketa in ba wasu kalilan daga cikin ‘yan jarida ba. Alhali kuwa yakamata ace mun fassarata da Hausa nan da nan (kamar yadda su Shehu Usumanu suke juyen litattafai da wakokin a da) don kowa ya san hakkinsa na samun bayanan da zai yi amfani dasu wajen yakar kasassabar da ake a gwamnati daga karamar hukuma har ta tarayya. Wannan hali na ko in kula ba zai haifar mana da alheri ba. Don haka yau ake juyin masa damu a Najeriya yadda aka ga dama. A karshe sai a barmu da fargar jaji da tunzuri na babu gaira babu dalili.

To da me muka dogara in bamu dogara da littafi ba? Akasarin lokacinmu muna bata shi ne a hira – mu maza. Mata kuwa suna gida suna ta girki, ko kallon fim, ko tadi da gulmace-gulmace irin nasu. A kowane gari, mutum zai kirga daba ta hira bila adadin. A nan ake sharhi kan siyasa, da gulman duk wanda ya wuce – mace ko namiji – da yada sharri cikin al’umma. Hatta wasanni malam bahaushe ya daina yi. Ga filayen nan an gina masa amma sai lalacewa suke, ko wasu su mora, shi ko ya yi ta fama da ciwon hawan jini, sa suga da sauransu.

In ko yana son sanin abu sabo, to sai ya dauki rediyo ya saurari shirin safe, ko na rana ko na dare a Muryar Amurka, Ko ta Jamus, ko BBC. A ganin malam bahaushe nan ne zai samu ilmi kan al’amura. Har ma yana yiwa kansa kirari cewa ya fi kowace al’umma sauraren rediyo a duniya. Amma abun kunya ba zai iya yiwa kansa kirari da cewa ya fi kowace karatu ba. Ya dogara da rediyo ne don tsabar lalaci tunda ba zai iya fidda kudi ya sayi littafi ko jarida ba. Ita kanta jarida ba zata ilmantar da mutum ba fiye da labarai da ra’ayi balle rediyo da ke fadin abu a takaice, a gurguje, ba tare da zurfafawa ba kamar yadda littafi ke yi. Ilmi sai a littafi, wanda dole a koyawa kwakwalwa abota da shi a koyaushe.

Ya kamata ‘yan Arewa su fara baiwa ilmi muhimmancin da ya kamaceshi. Su azuma wajen nemansa da farko, sannan su ci gaba da ingantashi ta hanyar karanta sabbin abubuwa da duniya ke ganowa. Daga nan sai su zurfafa wajen tunanin yadda za su yi amfani da ilmin wajen warware matsalolin da suka addabesu, daga nan har ma su yunkura wajen gano sabin abubuwa da duniya bata sani ba.

Wannan shi zai zama mataki na farko wajen fahimtar duniyar da muke ciki har ya kaimu ga tafiya kafada da kafada da sauran mutane, walau a nan gida Najeriya ko a kasashen waje. Dole ne mu raya al’adar karatu da magabatanmu suka bar mana, wacce ita ta sa muka kere saura a da har muka kafa dauloli da aka assasa akan ilmi lokacin da wasu suke rayuwar dabbobi a daji, suna cin mutane suna gudanar da mugayen al’adu. A yau, sun wucemu don sun baiwa ilmi muhimmanci, sun yi tsayin daka wajen gano shi, da kirkiro abubuwa dabam dabam da suka yi amfani da shi suka mamaye duniya.

A nan gida Najeriya ma idan bahaushe bai maida hankali kan ilmi ba, to zai zame leburan sauran ‘yan Najeriya wadanda suke kokarin kwarewa a fannoni dabam dabam na cigaba, shi kuwa an barshi da daba, inda yake gulma da yada sharri.

Yakamata dukkan ‘yanbokonmu su kasance suna sayen sabbin litattafai don wayar da kanunsu da al’ummarsu. A koyaushe, yakamata a samu danboko da sabon littafi ko’ina zai je yana karantawa wanda daga ciki zai fito da abubuwan da al’ummarsa zata amfana da shi. A shekara akalla kar ya gaza karanta litattafai 12, sabbi da nufin cigaba.

Hakanan kuma, duk danbokon da ke son amsa sunansa, yakamata ya daure ya tabbatar da yana amfani da dabarun rayuwar yau da kullum da aka koya masa a makaranta ko wandanda yake karantawa yau da kullum. Yakamata al’umma ta zame alkiblarsa, ba jin dadinsa da iyalansa ba kawai. Sauraren rediyo da karanta jaridu suna da amfaninsu, amma ba za su wadatar ba wajen baiwa al’umma alkibla da jagoranci da ke bukatar nazari mai zurfi.

In mun yi kokari, a lokaci kankani litattafai da karatu za su dawo Arewa, hakaza ilmi mai amfani da wanzar da shi a ko’ina. Ilmi shi ne kadai zai sa mu gane matsalolinmu da hanyoyin da zamu warwaresu. Wannan shi ne babin farko na jawo arziki wanda in ba shi aka bude ba, fatara kam za ta ci gaba da samun gindin zama har illa masha Allahu. Abun da za su biyo mata kuma na kasakanci, da lalacewa, da cututtuka, da zalunci, da bauta, za su cin mana, ko bajima ko badade.



6 June 2011