Total Pageviews

Friday, December 18, 2015

Doka Tushen Zaman Lafiya

6. DOKA, TUSHEN ZAMAN LAFIYA (Mutadaarak) ______________________________________

Nazarin Aruli:

Bahari: Mutadaarak
Kafa Maimaitau: Faa’ilun faa’ilun faa’ilun (5, 5, 5)
Fiɗa: - v - / - v - / - v -
____________________________

1. Na yaba Rabbi mai jin kira
 Jalla, Allahu mai gafara
 Kauda duk muguwar kaddara
 Ga ni bawa ina yin bara
   Ba mu doka a Nijeriya.

2. Zamani ne na yau zan faɗa
Kin biyayya jahala daɗa
Zuciya har idan ta kaɗa
Ba abun yi awa ai faɗa
  Babu zancen zaman lafiya.

3. Zan yi zance kamar shaguɓe
Yau fa doka mu san ta zube
Duk kasa ga shi an rarrabe
Masu mulki suna lalube
Yanda za mui zaman lafiya

4. Gaskiya zan faɗa ka’ida
 Lalube ba shi yin fa’ida
Lafiya za ta zo har gida
Babu karya bare za’ida
Gun Aliyu maso gaskiya.

5. In ka so zan kwatanta maka
 Lafiyar duniya nan duka
Yin gini ne cikin ayyuka
Ginshiki tubali bincika
  In da kyawu gini lafiya.
 
6. Tubali in ya bend ka jiya
 Du gini za ya zam laulaya
Ko siminti a ce bai jiya
Babu karfi tsayo zai wuya
Sai zubewa ga baki ɗaya.

7. Duk kasashe muhimmai gama
Masu yalwa da daɗin zama
 Cigabansu a kas har sama
La sihir kullaha innama
Sun bi dokarsu ba zamiya.

8. Ka’ida ce suke bi duka:
 Kora doka bisa kayuka
Martaba, dukiya, rayuka
In ka take su ka sha daka
  Rayuwa yari ba lafiya.

9. Kowane gunsu daidai shi ke
 Mai talauci biyayya ya ke
Maikuɗi, tajiri bai sake
In ya laifi hukunci ake
Martaba ba ta sa yafiya.

10. In kasa ka ga ta sunkuya
Ka ga manya suna yin tsiya
 Ba tsaron rai bare dukiya
Cin mutuncin mutum ba wuya
  Kar ka sa ran zaman lafiya.

11. Gu da dama a Ifrikiya
Sa kudanci na Sudaniya
 Har kasar tamu Nijeriya
 Libya sa Santa Ifrikiya
Babu doka bare gaskiya.

12. Larabawa mutan Eshiya
 Ga Yaman nan zuwa Syria
 Afghanistan haɗo Chechniya
Ran mutum sai ka ce kurciya
Hargitsi ba zaman lafiya.

13. Mun daɗewa da shubka kasa
Mun zata cigaban duk kasa
 An gina mu ko mun farfasa
 Mun ɓarar ba rabo mun rasa
  Sai nadamar marar gaskiya.

14. Farfaganda ta kanci: Ruwa!
Munka sha har muna yin rawa
Mun yi tatil muna yin juwa
Nan da nan munka wo mantuwa
Mun yi waka ta sharholiya:

15. “Yau talauci fa zai ɗaukaka
 “Dukiyarmu rabon muduka
 “Maida sarki abin caccaka
“Malami, tajiri su duka
  “Martaba sai a jamhuriya.

16. Keta doka ya zam ka’ida
 Gun mutane da yanci guda
 Kangarewa adon maigida
Kan jimawa gari sai kiɗa
Rusa mulki muna fariya.

17. Kan talakka kamar tsautsayi
 Ya yi mulkinsa mai laulayi
Tangaɗi, magiya, ga layi
Babu kishi abin tausayi
Cin amana da son danniya.

18. Babu doka ta kaya da rai
 Martaba babu sai dai garai
Maguɗi ba shi zaɓen kwarai
 Jahili ga shi nan sakarai
  Ba shi kaunar maso gaskiya.

19. Da yana son zaman lafiya
Sai ya zamto rikon gaskiya
 Sanya doka da yin tarbiya
Masu laifi su zam sun biya
Ka ji tushen zaman lafiya.

20. Sai mu bunkasa duk ayyuka
Baiwa yara abin ɗaukaka
Babu gilla da kwaya duka
Sai biyayya, rashin laifuka
  Duk ƙasa kwance sai lafiya.

21. Mu talakka batun gaskiya
Inda son rai cikin zuciya
Hargitsi za shi zo ba wuya
Bin mu doka zaman lafiya
Ka ji kalma batun gaskiya.

22. Mas’ala ko idan ta zaka
Kar mu saurin zama harzuka
 Mui ta haushi kamar karnuka
Keta doka muna hallaka
Rayuka, dukiya kun jiya?

23. Yanda doka ta ce kan’uwa
 Za mu tai inda mai unguwa
Hakimi ba bari har zuwa
Can ga sarkin kasa mui kuwa
Don muna son zaman lafiya.

24. In ko laifi akai wa kasa
Dukiya ko ko rai an rasa
Kotu ce za ta yanke masa
Rayuwa ka’ida ce musa
Hankali za mu zam lafiya.

25. Mui ta watsi da duk rarraba
Mui haɗewa da juna gaba
Mu jama’a zuwa shugaba
Rayuwa babu ko fargaba
Za ta dawo kamar can jiya.

26. In ko cewa muke mun kiya
Kowane zai bi son zuciya
Yi da gangan muna fariya
Babu doka a Nijeriya
Ture zancen zaman lafiya.

27. Masu laifi iri ɗai suke
Masu biro kisa ma suke
Shi da harbi ka bar bincike
Zuciya mai biɗar mallake
Duniya ba zaman lafiya.

28. Dukiya, martaba, rayuka
 Kar mu ɓata ukun su duka
Gun kalami mu bar zantuka
Duk amana mu zan mun rika
Mui ta himmar zaman lafiya

29. Nai kira yau ga Sarki ɗaya
Kai salama ga duk duniya
 Agazawa ga Nijeriya
 Don mu zamna cikin lafiya
Dukkanin mu ga baki ɗaya.

30. Zan takaita a gun nan haka
Ga talatin da ɗai baituka
Fa’ilun, Fa’ilun bincika
Gargaɗi gun mazo laifuka
Masu rushe zaman lafiya.

31. Nai kira Rabbi kai sallama
Kansa manzo daɗo sallama
Kan iyaye ka zan ka gama
Har da mu duk cikin sallama
Duniya, Lahira duk ɗaya.

Tammat walhamdulillah.

24 ga Fabrairu 2015

No comments: