Total Pageviews

Saturday, January 20, 2018

Arewa: Idan Ba Za Mu Girmama Doka Ba, Ba Za Mu Daina Ganin Bala'i Ba

Duka rikice-rikicen da muke gani a Arewacin Nijeriya da talaucin da ya yi katutu a cikinsa ba za su kau ba sai ran da muka gane muhimmancin doka da bin ta.
Ba yadda za a yi a ce za a bar jama'a da kungiyoyin addini kowa ya yi ganin damansa kuma kasa ta zauna lafiya. In mun yi magana game da tauye hakkin sauran jama'a da ake yi ta fuskar addini a yi caa a kanmu kamar mun aikata kaba'ira.
Don Allah menene amfanin toshe hanya ga matafiya da kowane dalili balle da sunan addini? Wañnan wulakanta bil'adama ne da rashin ganin kimarsa. Ga shi muna gani kullum a muzaharori da tawagar malamai a manyan tituna da tarukan kasa na addini kala-kala. Mutane da ke da'awar karatu amma tunaninsu kamar wadanda ke rayuwa a kungurmin daji? Wallahi wannan abin takaici ne.
Yanzu menene amfanin abin da ya faru a Zaria jiya, yake faruwa yanzu haka a Gellesu? Menene amfanin taron addini in zai jawo salwantar rai guda daya tak ma? Shin dole ne? Salla ne ko azumi ko aikin hajji? Wañnan abin an yi shi ba sau daya ba ba sau biyu ba, rayuka suna hallaka. Meye amfanin kwakwalwar da take kanmu idan ba za mu yi tunani da ita ba mu gane abu mai amfani da maras amfani, abu mai cutarwa da kuma maslaha, ko kuma cewa zaman lafiya ya fi komai? Me ya sa ba mu dau zubar da jini a kan komai ba har ta kai a ko yaushe ba mu damu da janyo falilin zubarsa ba alhali muna da'awar addini?
A ce har Shugaban Sojojin Kasa na Nijeriya zai wuce a ki ba shi hanya bai da ce da dabi'armu ta girmama na gaba da mu ba. Kuma a kasa gane cewa haka yana iya jawo salwantar rayuka kamar yadda ya jawo a baya abin mamaki ne ga kowane mai hankali, balle kuma an hada da jifa da sauransu.
Ina ga ba inda haka zai faru a kudu. Sam. Amma mu siyasar tawaye ta yi karfi a tsakaninmu har muna ganin babu babba ba yaro. Kowa muka ga dama za mu ci mar mutunci babu damuwa. Balle kuma an yi wa addini fassarar tawaye. Shi ke nan, mahaukaci ya hau kura.
Su mutanen da ke da matsala da tsarin da ake ciki yanzu suna iya yin kaura zuwa inda za su yi rayuwa irin wacce suke so. Wannan haka ya ke ko a nassi. Amma ka ce ba za ka yi biyayya ga hukuma ba kuma kana zaune a kasarta, ko a zamanin da wannan almara ce kawai. Zabi biyu ne kawai: ko dai ka yake ta ko kuma ka zauna lafiya da ita. Period. Wannan dokar duniya ce tun fil azal kuma ba za ta canza ba har ta nade.
Allah sarki! Ga yanki mai mutane masu basira amma barandanci na addini da rashin wayewa ya tukuikuye tunaninsu sun kasa yi wa kansu tanadin alheri ko sa samu cigaba su fita daga kangin talauci. Ga yanboko - manyansu da yaransu - su kuma barayi, bakaken azzalumai kuma maciya amana. Su ma ba su dau doka a kan komai ba. Ka rasa ina za ka waiga ka ga sa'ida.
Mu sani doka ita ce zaman lafiya. Zama lafiya kuma shi ne komai. In kowa ya yi kokarin bin ta sai a ci gaba. In an ki, oho, mu ne dawaman cikin bala'i alhali sauran kasar na cigaba.
Wannan sharhi nawa kila wasu su gan shi ya yi zafi. Zafi ne da ta bijiro daga takaickn halkn da wadanda kake so suke ciki. A ui hakiri. Wannan kuma kamar yadda Al-Mutanabbi ya ce abin da ya kamaci duk tsayayye ke nan. Ba Dan Arewan da ke jin dadin taasar da ake tafkawa na kashe-kashe a Zaria a yanzu haka. Amma dole ya yi takaicin yadda ko yaushe muke tsaga bango don kadangaru su shiga.
Na ga wasu har sun fara karkata maganar zuwa zancen kisan da ake yi wai ko bai fi tsare hanya laifi ba. To ba haka maganar take ba. Na yi sharhi ne kan rashin bin doka da yin abubuwa wadanda suke haddasa tashin hankali. Tabbas kisa babban laifi ne. Amma me zai sa mutum ya yi tsokanan da zai jawo kisa? Tsokana kadai na iya jawo yakin duniya. Mutum ya kafa kungiyarsa ya je Oran ko Saudia ya tsokani Babban Hafsan Sojar kasar ya ga abin da zai same shi. Kungiyar ma idan bata yarda da gwamnati ko doka ba ba za a bari ta wanzu ba bare har ta yi karfin da za ta yi tsokana a fili.
Allah mun tuba. Allah mun tuba. Ka fid da mu daga wannan annoba ko na bayanmu za su samu su rintsa.
Aliyu

No comments: